Jihohi 11 ne basu da wakilici a jerin sunayen ministocin da Tinubu ya turawa majalisa

Date:

Daga Hafsat Lawan Sheka

 

A jiya Alhamis ne shugaban kasa Bola Tinubu, ya aike da jerin sunayen ministoci 28 ga majalisar dattawan Nigeria, domin tantance su a kokarin da yake yi na cika wa’adin kwanaki 60 da kundin tsarin mulkin ƙasar ya kayyade masa.

 

Jaridar Kadaura24 ta yi nazari kan jerin sunayen wadanda aka aikawa majalisar, da kuma jihohin da suka fito, inda ta gano cewa jihohi 11 ba su da mutum ko daya a cikin sunayen ministocin da aka tura zuwa yanzu .

Talla

A cewar sashe na 147(3) na kuskwararren kundin tsarin mulkin Nigeria na 1999, “Shugaban kasa zai nada a kalla Minista daya daga kowace Jiha, wanda zai zama wakilin jiharsa a zauren majalisar zartarwar ta kasa .”

 

Bisa jerin sunayen da shugaban kasa ya aikewa majalisar, jihohin Katsina, Cross River, da Bauchi suna da ministoci bibiyu, yayin da jihohi 11kuma basu sami ko da mutum daya ba ya zuwa yanzu.

Ministoci: Dalilin da yasa Tinubu bai tura sunan kowa daga Kano ba

Jihohin goma sha daya sune Adamawa, Bayelsa, Gombe, Kano, Kebbi, Kogi, Plateau, Lagos, Osun, Yobe, da Zamfara.

Matan da aka nada a matsayin ministoci wadanda suka yi aure akan dauko su ne daga jihohinsu, in ban da Ngozi Okonjo-Iweala, wadda aka zaba a jihar Abia (jihar mijinta) a shekarar 2003.

Da dumi-dumi: Muhammad Bozoum ya Magantu Bayan yi Masa Juyin Mulki

Ga jerin sunayen ministocin da aka nada da jihohinsu:

Abubakar Momoh – Edo

Yusuf Maitama Tuggar – Bauchi

Ahmad Dangiwa – Katsina

Hanatu Musawa – Katsina

Uche Nnaji – Enugu

Betta Edu Cross – Rivers

Doris Uzoka – Imo

David Umahi – Ebonyi

Nyesom Wike – Rivers

Mohammed Badaru – Jigawa

Nasiru El-Rufai – Kaduna

Emperikpe Ekpo – Akwa Ibom

Nkiru Onyejiocha – Abia

Olubunmi Tunji-Ojo – Ondo

Stella Okotete – Delta

Uju Ohaneye – Anambra

Bello Mohammed Goronyo – Sokoto

Dele Alake – Ekiti

Lateef Fagbemi —Kwara

Mohammed Idris – Niger

Olawale Edun – Ogun

Adebayo Adelabu – Oyo

Imaan Sulaiman-Ibrahim – Nasarawa

Ali Pate – Bauchi

Joseph Utsev – Benue

Abubakar Kyari – Borno

John Enoh – Cross River

Sani Abubakar Danladi – Taraba

Ana sa ran shugaba Tinubu zai aika da karin jerin sunayen ga majalisar dattawa domin cika sharuddan tsarin mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...