Da dumi-dumi: Shugaban Majalisar Wakilai ya kaddamar da kwamitocin majalisar

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Tajudeen Abbas, kakakin majalisar wakilai, ya bayyana sunayen ‘yan majalisar da za su jagoranci kwamitoci 134 a zauren majalisar.

 

Abbas ya bayyana sunayen shugabannin kwamitocin da mataimakansu a zauren majalisar a ranar Alhamis.

Talla

Kundin tsarin mulkin Nigeria dai shi ne ya bayyana cewa yana daga cikin aikin yan majalisar su rika bibiyar aiyukan ɓangaren zartarwa ta hanyar kafa kwamitocin da zasu rika sanya idanu akan aiyukan ma’aikatu da Hukumomin gwamnati.

Yanzu-Yanzu: Majalisar Dattawa ta bayyana sunayen wadanda Tinubu zai nada Ministoci

Ga wasu daga cikin sunayen yan majalisar da zasu shugabanci kwamitocin sun hada da James Faleke (finance); Muktar Betara (FCT); Akin Alabi (works); Bamidele Salami (Public account); Idris Wase ( hukumar federal character); Leke Abejide (custom); Jimi Benson (defense); Ahmed Satomi (national security) da Yusuf Gagdi (navy).

Sauran su ne Alhassan Doguwa ( petroleum resources upstream); Ikenga Ugochinyere ( petroleum resources doenstream); Sada Soli (weter resources), da Wole Oke (judiciary).

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...