Za mu fara amfani da karfin doka wajen magance zubar da shara barkatai a Kano – MD REMASAB

Date:

Daga Kamal Umar Kurna

 

Shugaban hukumar kwashe shara da tsaftar muhalli ta jihar Kano Amb. Alhaji Ahmadu Haruna Zago, yace hukumar sa zata yi amfani da sashin dokar ma’aikatar wajen tursasawa tare da magance dabi’ar zubar da shara da tsakar dare a wuraren da basu kamata ba a jihar nan.

 

Shugaban ya bayyana hakan ne lokacin da yake tattaunawa da manema labarai sanda ma’aikatan hukumar suke tsaka da aikin kwashe sharar dake fagge ‘yan Alluna.

Talla

Ambasada Dan zago yace abin takaici ne yadda wasu suke bin tsakar dare suna jibge sharar akan titunan jihar nan da wuraren da basu dace ba musamman wuraren da aka kwashe sharar tun da farko.

Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya nada shugabannin wasu Ma’aikatun Lafiya a Kano

A bayanansu tunda farko mazauna kasuwar ta ‘yan fagge ‘yan Alluna sun yaba da yadda aikin kwashe sharar yake gudana a fadin jihar nan Koda dai wasu daga cikin su sun bayyana cewa kamata gwamnati ta gudanar da aikin tuntuni.

 

Daga cikin wuraren da hukumar kwashe sharar tayi aiki a yau sun hada da fagge ‘yan Alluna, karkashin gadar kasuwar Bata da New Road dake Unguwar Sabon Gari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...