Ku yawaita dashen itatuwa don kaucewa dumamar yanayi da kwararowar hamada – Sarkin Kano ya fadawa al’umma

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Mai martaba sarkin kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya bukaci al’ummar jihar kano dama kasa baki daya da su himmatu wajen dasa itatuwa don kaucewa kwararowar hamada.

 

” A irin wannan yanayi da ake fuskantar chanjin yanayi yana da kyau al’ummar mu su kaucewa sare bishiyoyi, a maimakon hakan ku mai da hankali wajen dashen itatuwa a muhallanku da sauran wuraren don bai gwamnati damar magance kwararowar hamada da dumamar yanayi”.

Talla

Mai Martaba Sarkin ya bukaci hakan ne lokacin da ya karbi ayarin shugabanin gudanarwa na Hukumar Kula da dazuzzuka da kwararowar hamada ta kasa karkashin jagorancin mataimakin shugaban hukumar Alhaji Auwalu Inusa Yusuf da suka kai masa ziyara a fadarsa.

Da dumi-dumi: Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin Hafsoshin tsaron Nigeria

Alhaji Aminu Ado Bayero, ya bayyana cewa ya zama wajibi ga al’ummar kasar nan musamman manoma dasu kaucewa sare itatuwa barkatai ba bisa ka’idaba.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran Masarautar kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa kadaura24.

Shi ma a nasa jawabin mataimakin shugaban hukumar Alhaji Auwalu Inusa Yusuf, yace sun kaiwa Sarkin ziyarar ne domin gaisuwar bangirma tare da neman tabarakin Sarki duba da cewa wannan ranace ta bikin dashen itatuwa ta duniya wadda ake gudanar da ita a duk shekara kuma a fadin duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...