Da dumi-dumi: Kotu Ta Dakatar Da Abba Gida-Gida Daga Rushe Gine-Ginen Jikin Badala

Date:

Babbar kotun jiha da ke Miller Road a nan Kano ta dakatar da gwamnantin Kano daga yin rusau a gine-ginen da ke jikin Badala akan titin zuwa jami’ar Bayero.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito gwamnatin jihar kano karkashin jagorancin Gwamna Engr Abba Kabir Yusuf ta sanyawa masu gine-gine a jikin badala alamar jan fenti wanda hakan ke alamta cewa kowanne lokaci za’a iya rushe gine-ginen, saboda abun da gwamnatin ta kirawo da cewa an yi gine-ginen ne ba bisa ƙa’ida ba.

Talla

Wannan na zuwa ne bayan da mamallaka wuraren suka roki kotun da ta duba halin da suke ciki, la’akari da cewar bu sa karya ka’ida ba wajen mallakar wuraren.

Cire Tallafin Mai: Za a yi ƙarin kuɗin burodi a Najeriya

Mai shari’a Hafsat Yahya Sani ce ta bayar da umarnin dakatarwar har sai kotu ta kammala nazari akan al’amarin.

 

Haka kuma ta sanya ranar alhamis 26 ga Oktoba mai zuwa a matsayin ranar da za a saurari shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...