Jerin sunayen ministoci: Shugaban APC, Adamu ya bayyana dalilin da ya sa Tinubu ya yi jinkiri fitar da ministoci

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Adamu, ya bayyana dalilin da ya sa aka dauki lokaci mai tsawo kafin shugaba Bola Tinubu ya bayyana sunayen sabbin ministocinsa.

 

Da yake magana a ranar Litinin a Abuja, yayin ganawarsa da shugabannin jam’iyyar APC a fadin kasar Nigeria, Adamu ya bayyana cewa Tinubu ya na tuntuba sosai kafin ya yanke shawarar sunayen wadanda zai zaba.

Talla

“Shugaban kasa yana tuntubar wadanda suka dace sosai kafin ya fito da wadanda zai nada a matsayin ministoci.

Sunayen Ministoci: Tsofaffin gwamnoni da yan takarda ne suka fi yawa cikin mutane 42 da Tinubu zai turawa Majalisa

“Za a fara fito da sunayen wadanda za’a nada a mukaman ministocin, sannan za’a tantance su kuma a sake mayarwa Shugaban kasa sunayen daga bisani kuma a bayyana sunayen .

“Kuma mai girma shugaban kasa zai nada ministocinsa a hukumance ya rantsar da su.

“Bayan ya yi hakan ne zai bayyana sunayensu tare da bayyana ma’aikatun da za’a tura su, hakan kuma a lokacin za’a gane zai rage ma’aikatu ko zai bar su a yadda suke.” in ji Adamau

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...