Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya baiwa Sheikh Aminu Daurawa mukami a hukumar Hisbah

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da nada Malam Aminu Ibrahim Daurawa a matsayin Kwamanda hukumar Hisba ta jiha.

 

Mataimakin gwamnan na musamman kan sabbin kafafen sadarwa na zamani, Salisu Hotoro, ne ya bayyana hakan a sashihin shafin sa na Facebook a yammacin wannan rana ta Litinin.

Talla

Sheikh Aminu Daurawa ya taba rike Mukamin lokacin mulkin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da Kuma lokacin mulkin Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

Sunayen Ministoci: Tsofaffin gwamnoni da yan takarda ne suka fi yawa cikin mutane 42 da Tinubu zai turawa Majalisa

Sheikh Daurawa dai ya bar kujerar Kwamandan hukumar Hisbah ne bayan samun sabini na siyasa tsakaninsu da tsohon gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje.

Malam Aminu Ibrahim Daurawa ne ya gudanar da tsarin auren zawarawa a hukumar lokacin da ya riƙe muƙamin a karon farko zamanin mulkin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...