Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya baiwa Sheikh Aminu Daurawa mukami a hukumar Hisbah

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da nada Malam Aminu Ibrahim Daurawa a matsayin Kwamanda hukumar Hisba ta jiha.

 

Mataimakin gwamnan na musamman kan sabbin kafafen sadarwa na zamani, Salisu Hotoro, ne ya bayyana hakan a sashihin shafin sa na Facebook a yammacin wannan rana ta Litinin.

Talla

Sheikh Aminu Daurawa ya taba rike Mukamin lokacin mulkin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da Kuma lokacin mulkin Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

Sunayen Ministoci: Tsofaffin gwamnoni da yan takarda ne suka fi yawa cikin mutane 42 da Tinubu zai turawa Majalisa

Sheikh Daurawa dai ya bar kujerar Kwamandan hukumar Hisbah ne bayan samun sabini na siyasa tsakaninsu da tsohon gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje.

Malam Aminu Ibrahim Daurawa ne ya gudanar da tsarin auren zawarawa a hukumar lokacin da ya riƙe muƙamin a karon farko zamanin mulkin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...