Da dumi-dumi: Majalisar wakilan Nigeria ta bayyana sunayen sauran shugabannin ta

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Shugaban majalisar wakilan Nigeria Tajudeen Abbas, a ranar Talata ya bayyana sunayen sabbin shugabannin majalisar wakilai ta 10.

Zargin Almundahana: Hukumar yaƙi da cin haci ta kama kwamishinan Ganduje da wasu mutane 5

Wadanda Shugaban majalisar ya sanar Sun hada da Julius Ihonvbere (APC – Edo, shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai), Halims Abdullahi (APC – Kogi, mataimakiyar shugaban masu rinjaye), Bello Kumo (APC – Gombe, mai tsawatarwa Chief Whip), Adewunmi Onanuga (APC – Ogun, mataimakin Mai tsawatarwa ).

Talla

Abbas ya kuma karanto wata wasika daga ɓangaren marasa rinjaye na majalisar, Inda suma suka bayyana sunayen wadanda zasu Jagorance su a majalisar.

Yanzu-Yanzu: Godswill Akpabio ya bayyana sunayen sauran Shugabannin Majalisar Dattawan Nigeria

Wasikar ta bayyana Kingsley Chinda (PDP, shugaban marasa rinjaye), Aliyu Madaki (NNPP, mataimakin shugaban marasa rinjaye), Ali Isah (PDP, mai tsawatarwa marasa rinjaye), da George Ebizimawo (Labour Party, mataimakin mai tsawatarwa marasa rinjaye).

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...