Babbar Sallah: Mataimakin gwamnan Kano ya taya Abba Gida-gida, Kwankwaso da Musulmi murna

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Kwamishinan kananan hukumomi da masarautu na jihar Kano, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ya taya gwamna Abba Kabir Yusuf da jagoran jam’iyyar NNPP na kasa Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da sauran musulmin jihar murnar zagayowar bukukuwan Sallah babba.

 

Sakon Barka da Sallah na Gwarzo na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaran sa, Ibrahim Garba Shuaibu ya fitar Kuma ya aikowa kadaura24 a ranar Laraba,

Tallah

 

Ya ce a yayin da al’ummar musulmi a fadin duniya ke gudanar da murnar zagayowar babbar sallah , akwai bukatar Musulmi su yi amfani da lokacin wajen son juna tare da sanya farin ciki a zukatan masoyansu.

Tsohon dan takarar gwamnan na jam’iyyar PDP ya taya al’umma Kano murnar Babba Sallah

Kwamishinan wanda shi ne mataimakin gwamnan jihar, ya bukaci al’ummar jihar da su marawa gwamnatin Gwamna Abba Kabir baya, yana mai cewa “Wannan gwamnatin ta daukacin al’ummar jihar ce. Dole ne mu ba shi goyon baya don cimma burin da ake so na maido da martabar jihar da ta bata”.

 

Ya kuma bukaci al’ummar musulmin jihar da su tabbatar da cewa suma sun tallafawa masu karamin karfi musamman a wannan lokaci na Sallah babba.

 

Tallah

Gwarzo ya yi kira ga mabiya addinin Musulunci da su yi amfani da bikin wajen da yi wa Najeriya addu’a musamman ta fuskar tsaro da tattalin arziki.

 

Kwamishinan ya sake jaddada alkawarin gwamnati mai ci na samar da shugabanci nagari da yanayi mai kyau ga ‘yan kasuwa domin zuba jari don bunkasa tattalin arzikin jihar da inganta rayuwar al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...