Allah yasan halin da muke ciki, don haka ku mayar da komai gare shi – Tinubu ya fadawa Yan Nigeria

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Shugaban ƙasar Najeriya Bola Tinubu ya amince da cewa Najeriya na fuskantar kalubale mai tarin yawa, amma kuma a cewarsa yana kokarin samar da hanyoyin magance matsalolin.

 

A cikin sanarwar da ya fitar na taya musulmin Najeriya murnar Barka da Sallah, Asiwaju Tinubu ya ce “Dole ne mu gode wa Allah Madaukakin Sarki da ya ba mu damar halartar wata Sallar Idi”.

Tallah

Ya ƙara da cewa Allah ba ya ɗora wa mutum abin da ba zai iya ɗauka ba.”

“Allah Ya san halin da ƴan Najeriya ke ciki kuma zai kawo musu sauƙi.”

Jerin gwanon motocin Tinubu ya haifar da cece-kuce a Nigeria

Sannan ya buƙaci al’umma da su yarda cewa ƙasar za ta gyaru, su kuma haɗa hannu wajen cimma nasarar hakan.

Ya kara da cewa gwamnatinsa ta fara neman hanyar magance matsalolin da ke addabar kasar, ta hanyar shawarwarin da suke samu daga wajen kwararru don gyara tattalin arziƙi da kuma kawarda duk wani cikas da zai hana bunƙasar Najeriya.

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...