Yanzu-Yanzu: Tinubu ya rushe majalisun gudanarwar Hukumomi, ma’aikatu da kamfanonin gwamnatin tarayya

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da rushe dukkanin majalisun gudanarwa na hukumomi da ma’aikatu, cibiyoyi da kamfanonin gwamnatin tarayya, ba tare da bata lokaci ba.

 

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Daraktan yada labarai na ofishin sakataren gwamnatin tarayya Willie Bassey a daren ranar Litinin a Abuja.

Da dumi-dumi: Tinubu ya sauke Hafsoshin tsaron Nigeria , ya kuma nada sabbi

Sanarwar ta ce, hakan yayi dai-dai da karfin ikon da kundin tsarin mulkin kasar ya baiwa shugaban kasa don amfanin jama’a.

Yanzu-Yanzu: Abba Gida-gida ya sake sabbin nade-naden mukamai

‘’Rushewar ba ta shafi kwamitoci da kuma Majalisun da aka tsara a Jadawali na Uku, Sashi na 1, Sashi na 153 (i) na Kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya na 1999 da aka yi wa kwaskwarima ba,’’ in ji sanarwar.

Dangane da wannan an umarci shugabannin ma’aikatu, Hukumomi, Cibiyoyi, da Kamfanonin Gwamnatin tarayya da cewa yanzu duk abun da zasu yi wanda zai majalisar gudanarwar su ta sani to, manyan Sakatarorin ma’aikatun su turawa Shugaban kasa ta karkashin ofishin sakataren gwamnatin tarayya.

Tallah

” Don haka, dukkan Ma’aikatu su tabbatar da bin wannan umurnin da zai fara aiki daga ranar Juma’a 16 ga watan Yuni, 2023″.

An umurci manyan sakatarorin da su sanar da shugabannin hukumomin da abin ya shafa a karkashin kulawar ma’aikatu/Ofisoshinsu domin a su bi umarnin cikin gaggawa .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...