Bayan komarwasa makarantar Islamiyya dattijo dan shekaru 60 ya sauke Al’qur’ani a Kano

Date:

Daga Kamal Yakubu Ali

 

Wani malamin addinin musulunci a kano sheikh Bashir Bakin Ruwa, ya bukaci iyaye da su kara maida hankali wajan tallafawa makarantun addinin musulunci duba da irin gudunmawar da suke bayarwa wajan samarda al’umma ta gari .

 

Sheik Bakin Ruwa ya bayyana hakan ne yayin bikin saukar karatun alkurani mai girma na daliban makarantar Raudatul kur’ani murattal bangaren Asuba da ummahatu karo na 2 na dalibai 17 wanda ya gudana a farfajiyar makarantar dake unguwar mai Aduwa dake karamar hukumar Dala.

Yanzu-Yanzu: Abba Gida-gida ya sake sabbin nade-naden mukamai

Sheikh Bakin Ruwa yace marigayi sheikh Abubakar Ramadan shi ne ya Assasa wannan makaranta domin yada ilimin addini musulunci da samar da mahaddatan alkurani da kuma kara chusa kaunar Annabi sallallah Alaihi wasallam da sahabbansa a zukatan al’ummar Musulmi .

Ya bukaci daliban dasu kara zage damtse wajan neman ilimi a fannoni daban-daban na rayuwa, domin samun kyakyawar rayuwa a duniya da lahira.

Tallah

Wasu Daga cikin daliban da suka samu sasarar saukar karatun alkurani sun hadar da Muhammad musa Dattijo Mai kimanin shekaru 60 da sauran manyan mutane, inda suka bayyana cewa tsofa bai hana so zuwa makaranta ba, kuma sun samu

Taron ya samu halarta al’umma da dama wadanda suka hadar da Alhaj Bature yahaya da sharif Auwal mahir sharif bala da sauran manyan limaman dake fadin jahar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...