Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Kano ta bayyana dalilin da yasa ta rushe shatale-talen gidan gwamnati

Date:

Daga Auwalu Alhassan Kademi

 

Gwamnatin jihar Kano ta ce rushe shatale-talen dake Kofar gidan gwamnatin jihar ne domin amfanin jama’a.

 

Kafin wannan aikin, gwamnati ta tuntubi kwararrun Injiniyoyi a fannonin da suka dace wadanda suka tabbatar da cewa ginin shatale-talen ba shi da inganci kuma akwai yiwuwar zai iya rugujewa ta 2024.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24.

Hotuna: yadda Aka rushe shatale-talen dake Kofar gidan gwamnatin kano

Wannan ya faru ne saboda ana yin shi da kayan aiki marasa inganci, hakan tasa dole a rushe shi don sake gina wani wanda zai dace da Kofar gidan gwamnatin kano.

 

Har ila yau, shatale-talen ya yi tsayi da yawa, wanda hakan tasa yake kawo barazana ga sha’anin tsaron gidan domin yana hana na’urorin tsaro dake gidan yin aikin su yadda ya kamata.

Bugu da ƙari, yana haifar da cunkoson ababen hawa a yankin saboda girmansa, tare da hana direbobi gano abun da ke gabansu.

Gwamnatin ta bayyana cewa ya zama dole ta rushe shatale-talen domin sake gina wani cikin gaggawa da kuma rage masa tsaho don tabbatar da ganin kofar gidan gwamnati da kare lafiyar masu ababen hawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...