An kama ma’aikatan majalisa da hadimai bisa satar kaya a majalisar tarayyar Nigeria

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Jami’an tsaro da ke aiki a harabar majalisar tarayyar Nigeria da ke Abuja, sun kama wasu hadiman ‘yan majalisa da ma’aikatan majalisar da laifin sata da kwashe wasu kayayyaki masu daraja a ofisoshin ƴan majalisa.

Sunday PUNCH ta tattaro cewa ‘yan majalisar dattawa da ta wakilai masu barin gado da wadanda suka sake cin zaɓe na ƙoƙarin fitar da tsofaffin kayayyakin ofisoshin su don saka sabbin kamar yadda ya ke a al’adar majalisar ta ke.

Nigeria Air: Dan majalisar da yace mun yi Damfara sai da ya nemi kaso 5 – Sirika

Wasu daga cikin kayayyakin sun hada da na’urorin talabijin, kantocin ajiye littattafai, na’urorin lantarki, kwamfutoci, firintoci, kayan daki, na’urorin sanyaya daki, kafet, da na’urorin wutar lantarki na doka.

 

Sai dai jami’an tsaro da harabar majalisar dokokin kasar sun cafke wasu daga cikin mataimakan ‘yan majalisar bisa yunkurin fitar da wasu kayayyaki ba tare da izini ba.

A cewar majiyoyi da dama, an kama wadanda ake zargin ne a lokacin da su ke kokarin ficewa daga cikin harabar ba tare da takardar izinin fita da kayayyakin ba.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Sajan mai kula da Majalisar, Chuks Obaloje, ya tabbatar da faruwar lamarin, amma bai iya bayar da cikakken bayani ba.

Majalisa ta 10: Jam’iyyar PDP ta yi zargin ana shirin kama ‘Yan Majalisarta

“Eh, an kama wasu mutane ne a yayin da suke kokarin fita da wasu kayayyaki daga Majalisar Dokoki ta kasa. Amma ban kasance kan aiki a ranar da abin ya faru ba, don haka ba zan iya ba ku cikakken bayani ba. Sai dai a tuntubi Sashen Laifuffuka na Majalisar Tarayya,” Obaloje ya shaida wa wakilin SUNDAY PUNCH a lokacin da aka tuntube shi a ranar Juma’a.

Jami’in ‘yan sanda mai kula da harabar majalisar dokokin kasar, Alex Annagu ya ki cewa komai kan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...