Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa
Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama na Nigeria, Sanata Hadi Sirika, ya zargi dan majalisar da ya bayyana Jirgin Sama na Nigeria Air a matsayin damfara da neman kaso biyar hannun jarin Kamfanin Jirgin Najeriya.
A zaman Jin ra’ayoyin al’umma da majalisar wakilai ta yi, shugaban kwamitin majalisar kan harkokin sufurin jiragen sama, Nnolim Nnaji, ya bayyana kaddamar da jirgin Najeriya Air a matsayin yaudara.
Da dumi-dumi: Da na sami Kwankwaso a fadar shugaban kasa da na dalla masa Mari – Ganduje
Ya zabo ramuka a cikin aikin, inda ya soki Gwamnatin Tarayya kan abin da ya bayyana da rashin tafiyar da shi.
Amma da yake ganawa da gidan talabijin na ARISE a ranar Lahadi, Sirika ya ce dan majalisar ya tuntube shi ya nemi a ba shi kashi biyar na hannun jarin kamfanin jirgin saman da “shi da jama’arsa”.