Yayin da aka dakatar da Emefiele darajar Naira ta sake faduwa

Date:

Daga Zainab Isa Muhammad

 

Darajar naira ta ƙara yin ƙasa a kasuwar canji da gwamnati ke amfani da ita ta Investors and Exporters (I&E) a ranar Juma’a, yayin da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya dakatar da Gwamnan Babban Banki Godwin Emefiele.

 

Jaridar Punch a Najeriyar ta ruwaito cewa kasuwar ta tashi a ranar Juma’a ana canzar da dala ɗaya kan naira 471.32.

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu ya dakatar da Gwamnan CBN, Emefiele

Rahoton ya ƙara da cewa da farko nairar ta ɗan ragu da kwabo 64, idan aka kwatanta da darajarta ta 469.50 a ranar Alhamis. Sai dai kuma ta ƙara faɗuwa har zuwa 471.32 kan dala ɗaya.

Da dumi-dumi: Kwankwaso ya bayyana abubuwan da suka tattauna da Shugaba Tinubu

Bola Tinubu ya dakatar da gwamnan bankin ne nan take cikin wata sanarwa, inda aka umarce shi da ya miƙa ragamar CBN ɗin ga mataimakin gwamna mai kula da harkokin gudanarwa, Folashodun Adebisi.

 

Mista Adebisi zai kasance muƙaddashin gwamna har sai an kammala binciken zarge-zarge a kan Emefiele da kuma sauye-sauye a bangaren kuɗi, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...