Gwamnan CBN Emefiele baya hannun mu – DSS

Date:

Daga

 

Hukumar tsaron farin kaya a Najeriya ta DSS ta ce yanzu haka ba ta tsare da tsohon Gwamnan Babban Banki (CBN) Godwin Emefiele.

Tun a daren jiya Juma’a wasu rahotanni suka ce jami’an tsaron sun yi awon gaba da shi jim kaɗan bayan Shugaba Bola Tinubu ya dakatar da shi daga muƙaminsa.

 

“Yanzu haka, Emefiele ba ya tare da mu,” in ji hukumar cikin wani saƙon Twitter.

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu ya dakatar da Gwamnan CBN, Emefiele

Ba wannan ne karon farko da rahotanni ke alaƙanta tsohon gwamnan da DSS ba, musamman tun bayan da ya ƙaddamar da shirin sauya takardun naira da kuma rage yawan ganin kuɗin a hannun mutane bisa amincewar tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

Da dumi-dumi: Kwankwaso ya bayyana abubuwan da suka tattauna da Shugaba Tinubu

Bola Tinubu ya dakatar da gwamnan bankin ne nan take cikin wata sanarwa, inda aka umarce shi da ya miƙa ragamar CBN ɗin ga mataimakin gwamna mai kula da harkokin gudanarwa, Folashodun Adebisi.

Mista Adebisi zai kasance muƙaddashin gwamna har sai an kammala binciken zarge-zarge a kan Emefiele da kuma sauye-sauye a bangaren kuɗi, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...