Janye tallafin mai: Masu gidajen mai ne suka jefa al’umma a wahala – Falakin Shinkafi

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Wani basarake mai rajin samar da sauƙi ga al’umma Amb. (Dr) Yunusa Yusuf Hamza Falakin Shinkafi ya ƙalubalanci masu gidajen da suke sayar da tsohon man fetur din da suka sayo da tsohon farashi akan sabon farashi.

 

” Wannan matakin da aka dauka babu Shakka zai sanya masu karamin karfi a cikin mawuyacin hali, saboda zai taba bangarori daban-daban na rayuwar al’umma musamman kayan masarufi da suka zama wajibi ga kowanne Dan Adam”. Inji shi

Falakin Shinkafin ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da jaridar kadaura24 a Kano.

Da dumi-dumi: Gwamnan jihar Kano ya kuma sanar da sabbin nada-naden mukamai

” A baya NNPC ta fadawa mutanen Nigeria cewa, tana da man da za’a iya amfani da shi har nan da watanni uku masu zuwa, don haka ban ga dalilin da zai sa a fara sayarwa yan Nigeria da tsohon man a sabon farashin ba”. Inji Amb. Yunusa Yusuf Hamza

Falakin Shinkafin wanda kuma shi ne Sardaunan matasan arewacin Nigeria ya bukaci gwamnatin Shugaban kasa Bola Tinubu Tinubu da ta ɗauki matakan da suka dace, don saukaka al’ummar Nigeria.

Yace su kuma masu gidajen mai suma ya kama su ji tsoron Allah, su kuma sani cewa sai Allah ya tambayesu kan mawuyacin halin da suka jefa yan Nigeria a ciki, saboda tsohon man da gwamnati ta biya masa tallafi suke sayarwa al’umma a kan sabon farashi na Naira 540 ko ma sama da haka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...