CBN ya Musanta labarin karya darajar Naira

Date:

 

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya musanta wani rahoto da ake yadawa cewa ya karya darajar Nigeria zuwa naira 630 a kan dala ɗaya.

Wata sanarwa da muƙaddashin darektan sadarwa na bankin, Isa AbdulMumin, ya fitar ya ce ko a jiya Laraba ma an sayar da kuɗin ne a kan naira 465 kan kowace dala saɓanin abin da wancan rahoton ya ce naira 630.

Da dumi-dumi: Gwamnan jihar Kano ya kuma sanar da sabbin nada-naden mukamai

Sanarwar ta ce rahoton da wata jarida ta yi wanda ta ce ta samu bayaninsa ne ita kadai yana cike ne da karerayi da kuma jahilcin rashin sanin yadda kasuwar hadadar kudaden waje ta Najeriya take.

Darektan ya jaddada matsayar bankin a kan lamarin inda ya ce ko a safiyar yau an sayar da naira 465 a kan dala ɗaya.

Bankin ya shawarci jama’a da su yi watsi da rahoton wannan jarida da cewa ta yi ne da nufin haddasa firgici a kasuwar musayar kuɗaden.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...