KAYYASA! : Awanni kadan kafin saukarsa, Ganduje ya Rantsar da Sabon kwamishina

Date:

Daga Kabiru Yusuf

Awanni kadan kafin ya sauka gwamnan jihar Kano mai barin gado Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya rantsar da sabon kwamishina a hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar kano KANSEC.

 

Kwamishinan shari’a na jihar Kano Barr. M A Lawan ne ya rantsar da sabon kwamishinan mai suna Abdullah Abba Sumaila, yayin taron majalisar zartarwar jiha na ƙarshe wanda ya gudana daren jiya a gidan gwamnatin kano.

 

Da yake jawabi bayan rantsar da sabon kwamishinan gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya ce an rantsar da kwamishinan ne bayan majalisar dokokin jihar kano ta tantance tare da Amincewa da nada shi a matsayin kwamishina.

 

” Muna fata zaka yi aikin ka yadda ya dace saboda muhimmancin da hukumar zabe take da shi musamman wajen shirya zaben kananan hukumomi a jihar kano”.

 

An dai rantsar da sabon kwamishinan ne awanni kasa da 48 a rantsar da sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar kano Engr. Abba Kabir Yusuf.

 

Sai dai mukamin kwamishina irin wannan na wannan hukumar ba kamar sauran kwamishinoni na siyasa da aka Sani ba , domin shi wa’adi ne da shi na kamar yadda doka ta gindaya .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...