Ganduje ya bude Ofishin Yan Sanda na zamani irinsa na farko a Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana na’urorin zamani a matsayin wadanda suke taimakawa wajen magance aiyukan bata gari, Saboda cigaban da aka samu .

 

” Saboda cigaban zamani da aka samu a duniya yasa gwamnatin mu ta samar da na’urorin zamani domin dakile aiyukan bata gari da Kuma kama Masu laifi a jihar Kano , wanda hakan yasa muka Sami nasarorin da muka samu a tsahon shekaru 8 na mulki na”. Inji Ganduje

Shafukan sada zumunta na da hadari ga lafiyar matasa – Masana

Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi yayin bude sabon ofishin yan sanda dake unguwar Rijiyar Zaki a karamar hukumar Ungoggo a Kano.

Ganduje wanda Sakataren gwamnatin jihar kano Alhaji Usman Alhaji ya wakilta ya yabawa Shugaban karamar hukumar Ungoggo Abdullahi Garba Ramat saboda kokarin da yake na bada gudunmawa don inganta tsaro a yankin da jihar kano baki daya.

Ya bukaci jami’an yan sanda da zasu aiki a sabon ofishin yan sandan na zamani da su yi amfani da Sabbin na’urorin da aka Sanya yadda ya dace don cigaba da samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

A jawabinsa tun da fari Shugaban Karamar Hukumar Ungoggo Abdullahi Garba Ramat ya ce bayan gini na zamani da aka yiwa ofishin yan sandan, an Sanya na’urorin zamani don saukaka aiyukan yan sanda da kuma magance matsalolin tsaro a yankin.

Sh ma a nasa jawabin kwamishinan yan sanda na jihar kano CP Muhammad Usaini Gumel ya yaba da Samar da sabon ofishin yan sandan, tare da bada tabbacin zasu yi kyakyawan amfani da na’urorin domin dakile aiyukan bata gari a yankin da kana baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...