Cutar Kwalara ta ɓarke a ƙasashen Afirka 15 – WHO

Date:

 

Hukumar lafiya ta duniya, WHO ta ce cutar kwalara ta barke a kasashen Afirka guda 15 ciki har da Afirka ta Kudu.

 

A ciki akwai kuma Jamhuriyar Dumukuradiyyar Kongo (DRC) da Eswatini da Mozambique da Kenya da kuma Zimbabwe.

 

Hukumar ta bayyana hakan ne bayan da mutum 15 ciki har da karamin yaro dan shekara uku suka mutu a Afirka ta Kudu a sanadiiyar kamuwa da cutar wadda ta fara mako daya da ya wuce.

 

Akwai kuma wasu mutanen sama da 30 da ke kwance a asibiti a cikin mawuyacin hali a kasar ta Afirka ta Kudu.

 

Hukumar ta WHO ta kuma ce Malawi ce ta fi yawan mutanen da suka kamu da cutar.

 

Su kuwa hukumomin Afirak ta Kudu sun ce an dauki tsauraran matakai a iyakokin shiga kasar domin hana masu dauke da cutar shiga.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...