29 May: Amuruka ta bayyana wakilan da za su halarci rantsar da Tinubu

Date:

Daga Safiyanu Dantala Jobawa

 

Shugaba Joe Biden, na Amurka ya bayyana sunayen wakilan gwamnatinsa da za su haraci rantsar da sabon shugaban Najeriya mai jiran-gado, Bola Tinubu, ranar Litinin 29 ga watannan na Mayu a Abuja.

 

A wata sanarwa daga Biden wadda aka sanya a shafin intanet na fadar gwamnatin Amurkar, White House jiya Litinin da daddare, shugaban ya sanar da tawagar mutum tara da za ta halarci taron.

 

Tawagar ta Amurka za ta kasance karkashin jagorancin Ministar Gidaje da Raya Birane, Marcia L. Fudge.

 

Ana sa ran halartar shugabannin kasashen duniya na da da wadanda ke kan mulki da jami’an diflomasiyya da shugabannin hukumomin duniya da wakilan gwamnatocin kasashe.

 

Za a rantsar da Tinubu tsohon gwamnan jihar Lagos a matsayin shugaban Najeriya na 16, a ranar ta 29 a dandalin taro na Eagle Square da ke Abuja

 

Tun daga ranar Alhamis za a fara gudanar da bikin inda Shugaba Muhammadu Buhari mai barin-gado zai bai wa Tinubun lambar girmamawa mafi girma ta Najeriya wato GCFR (Grand Commander of the Order of the Federal Republic) wadda ake ba shugaban kasa, sai kuma mataimakinsa Kashim Shettima wanda za a ba shi lambar da ke bi mata ta GCON ( Grand Commander of Order of the Niger).

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...