Daga Rukayya Abdullahi Maida
Gwamnan jihar kano Abdullahi Umar Ganduje, ya bayar da umarni ga dukkanin Kwamishinoni da shugabannin Ma’aikatu da hukumomin gwamnatin kano da su ajiye mukamansu nan da ranar juma’a 26 ga wannan wata.
Kadaura24 ta rawaito hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ofishin sakataren gwamnatin Kano ya fitar mai dauke da sa hannun babbar sakatariyar ofishin Bilkisu Shehu Maimota.
Sanarwar ta kuma bukaci masu mukaman Siyasa da su mika ragamar ma’aikatunsu ga manyan Sakatarorin gwamnatin ko daraktoci ma’aikatunsu tare da kayan gwamnati dake wurinsu.
” Wadanda mukamin da aka basu yana da wa’adin sauka to su cigaba da rike mukamansu dai-dai da yadda dokokin da suka nada su suka tanada”. A cewar sanarwar
Mutane huɗu sun rasu a fashewar tukunyar gas a Sokoto
Sanarwar ta godewa daukacin wadanda suka rike mukaman saboda irin gudunmawar da suka baiwa gwamnatinsa da kuma irin nasarorin da ya samu tsahon shekaru 8 da suka gabata.
Sanarwar ta ce ajiye mukaman ya hadar da kwamishinoni da masu baiwa gwamna shawara da mataimakan gwamna na musamman da manyan mataimaka na musamman ga gwamna da duk Masu rike da mukaman Siyasa.
Idan za’a iya tunawa a ranar Litinin 29 ga watan mayu za’a rantsar da sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar kano Engr. Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP.