Ƙungiyar ɗalibai ta yi ƙorafi ga gwamnatin tarayya kan littattafan firamare da ke koyar da batsa

Date:

Kungiyar Daliba Musulmi ta Ƙasa, wato MSSN ta bayyana damuwarta kan sanya abubuwan da suka danganci jima’i a cikin wasu litattafan firamare da sakandare da ake yadawa a Nijeriya.

A wasika mai taken “Saka bayanan Jima’i da Luwadi a Littattafan Firamare da Sakandare na Najeriya: Barazana ga tarbiyya da kuma xin zarafin al’adu/addini,” an aika ta zuwa ga ministan ilimi, Adamu Adamu.

Wasikar, mai dauke da sa hannun kodinetan kungiyar, Qaasim Odedeji, da babban sakataren kungiyar, Abdul Jalil Abdur Razaq, su ka sanyawa hannu kuma mai kwanan wata 15 ga watan Mayu, ta nuna rashin jin dadin ƙungiyar kan yadda ake yaɗa ilimin jima’i a wasu litattafan Lissafi, Turanci, da zamantakewa da ake amfani da su a yawancin makarantun sakandaren Nijeriya.

“Mun yi mamakin abubuwan da ke cikin wasu litattafan Lissafi, Turanci, da Kimiyyar zamantakewa da ake amfani da su a yawancin makarantun sakandaren Najeriya a yau.

An gurɓata waɗannan littattafan na karatu har sun haɗa da abubuwan lalata da batsa don lalata da yara ƙanana.

Da take bayar da misalai, kungiyar ta ce wata tambayar da ake yi wa daliban firamare a wani littafin lissafi ita ce “kwaroron roba 20 a tara da kwaroron roba 5 sannan a ɗebe kwaroron roba 2 daidai ya ke da.”

Sun kara da cewa wasu daga cikin litattafan suna yaɗa zubar da ciki, LGBT, wasa da al’aura, da jima’i cikin kariya.

Sun yi kira ga ma’aikatar ilimi da ta gaggauta gudanar da bincike kan lamarin tare da tabbatar da cewa litattafan da ake amfani da su a makarantun Najeriya ba su da abubuwan da ke da illa ga tarbiyyar matasa dalibai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...