Mutane huɗu sun rasu a fashewar tukunyar gas a Sokoto

Date:

Akalla kimanin mutane huɗu ne suka rasu sakamakon fashewar tukunyar iskar gas a wani shagon mai akin walda da ke karamar hukumar Isa ta jihar Sokoto.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar DSP Sanusi Abubakar ya tabbatar wa Gidan Talabijin na Channels cewa fashewar ta auku ne a ranar Lahadi.

Sai dai ya ce fashewar ba ta da nasaba da rashin tsaro da ake fama da shi a yankin, illa tukunyar gas ce kawai ta fashe.

DSP Sanusi ya ce ba ya ga mutum huɗu da suka rasu, akwai wasu mutum uku da suka jikkata kuma suna karɓar magani a asibiti.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...