Goodluck Jonathan ya bayyana abin da yake hana shi barci a fadar shugaban kasa

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Tsohon shugaban kasar Nigeria Goodluck Jonathan ya ce rashin tsaro ya sa shi “mummunan ciwon kai” a lokacin da yake rike da shugabancin Najeriya.

 

Ya bayyana haka ne a lokacin kaddamar da aikin titin mai tsawon kilomita 22 a jihar Taraba.

A cewarsa, yana kwana bai yi barci ba sakamakon kokarinsa na magance matsalar tsaro a wancan lokaci.

Tsohon shugaban kasar ya bukaci al’ummar jihar da su zauna lafiya domin a samu ci gaba.

Jonathan, wanda ya bayyana cewa tsaro yana hannun jama’a, ya bayyana farin cikinsa yadda a hankali Taraba ke komawa cikin kyakkyawan yanayin zaman lafiya da juna.

“Lokacin da nake shugaban Najeriya, rashin tsaro ya sa na kasa barci. Wani lokaci ma yayin da nake coci, ADC na ya kan kawo waya ta ya nuna min yadda ake kashe mutane ko sace mutane, kuma hakan yana da na sami ciwon kai kuma na kasa barci.”

“Lokacin da na shigo filin jirgin sama na Jalingo, da na ga Daraktan DSS, sai na yi sauri na tambaye shi, ‘Yaya akai jami’an tsaron jihar Taraba suke da himma?’ sai ya ce min mutanen ‘Taraba na son zaman lafiya da kwanciyar hankali’,” a cewar Jonathan

Jonathan ya zama shugaban Najeriya daga 2010 zuwa 2015

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...