Doguwa ya janye daga takarar shugabancin majalisa, zai marawa wani baya

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai, Alhassan Ado Doguwa ya janye kudirinsa na neman shugabancin majalisar wakilai ta 10, Inda ya bayyana goyon bayansa ga Tajudeen Abbas.

 

Doguwa ya jagoranci wasu ‘yan takara biyu Abubakar Makki da Tunji Oluwuyi, inda suka janye daga takararsu a ranar Larabar da ta gabata yayin wani taro da kungiyar hadin gwiwa ta shirya, kamar yadda rahoton Daily Post ya nuna.

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano domin kaddamar da wasu aiyuka – Ganduje

Idan dai ba a manta ba kadaura24 ta rawaito jam’iyyar APC mai mulki ta amince da Abbas da Ben Kalu a matsayin shugaban majalisar da mataimakinsa, lamarin da ya haifar da cheche-ku ce a tsakanin ‘yan takarar.

A baya dai Doguwa ya bi sahun wasu masu kalubalantar Abbas, Amma kuma yanzu ya aminta zai marasa masa baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...