Akwai fargabar karatun daliban da dama a Jami’ar Yusuf Maitama Sule ya Sami tasgaro – Shugabar Dalibai

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

Karatun wasu daga cikin daliban jami’ar Yusuf Maitama Sule  zai iya tsaya, sakamakon gaza biyan kudin makarantar da aka saba biya duk shekara a sabon zangon karatu.

 

“Mun karɓi koken dalibai da dama wadanda yawancinsu ‘yan aji uku da aji hudu ne cewar sun yi iya bakin kokarinsu domin su biyan kudin makarantar Amma abun ya ci tura, kuma babu shakka duk wanda aka rufe bai biya kudinsa akwai yiwuwar ya shiga wani hali maras dadi sakamakon dakatar da karatunsa”.

Shugabar kungiyar dalibai ‘yan asalin jihar kano dake karatu jami’ar Amb. Habiba Usman Hassan ce ya bayyana hakan yayin wata ganawa da ta yi da kadaura24.

Sarkin Karaye ya sake baiwa kanin Kwankwaso Sarauta

Tace dalibai da dama a baya sun shiga cikin mawuyacin hali sakamakon dakatar da karatunsu , hakan ce tasa ta ga dacewar a matsayinta ta shugaba ta nemar musu tallafi daga al’ummar jihar kano don inganta rayuwar su da kuma kare rayuwar su daga rugujewa.

 

“Gaskiya Hukumar jami’an ta yi iya kokarin ta domin ta karawa ɗaliban wa’adi, amma duk da haka akwai dalibai da dama da suka gaza biyan kudin, don haka muke rikon shugabanni da masu hannu da shuni da su tallafawa wadannan dalibai don ceto rayuwar su”.inji Amb. Habiba Usman Hassan

 

Amb. Habiba Usman wadda ake yiwa lakabi da Garkuwar dalibai tace idan aka sami Masu taimakawa Wadancan dalibai zasu iya tuntubar hukumar jami’ar ko kuma kungiyar dalibai yan asalin jihar kano domin ganin an tallafawa wadanda abun ya shafa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...