Majalisa ta 10: APC ta bayyana sunayen wadanda ta ke so su zama shugabannin majalisar

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Jam’iyyar APC ta fitar da tsarin shiyya-shiyya na mukaman shugabannin da take son su jagoranci a majalisar kasa ta 10 da ke tafe.

 

Babban Kwamitin uwar ayyuka jam’iyyar APC mai mulki ta amince da Sanata Godswill Akpabio daga Kudu maso Kudu da Jubril Barau daga Arewa-maso-Yamma a matsayin shugaban majalisar dattawa da mataimakinsa a majalisa ta10 .

Haka kuma, shugabannin jam’iyyar APC na kasa sun amince da zabin Hon. Tajudeen Abbas daga Arewa-maso-Yamma da Hon. Benjamin Kalu daga Kudu-maso-Gabas a matsayin kakakin majalisa da mataimakinsa a majalisar wakilai mai zuwa.

Kotun sauraren kararrakin zaben shugaba ta bada tabbacin yi wa kowa adalci

Jam’iyyar APC ta bayyana matsayin ta ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren yada labaran jam’iyyar na kasa, Felix Morka, bayan wani taron jam’iyyar na NWC a hedikwatar jam’iyyar APC da ke Abuja a ranar Litinin, don goya baya ga sakamakon ganawar da suka yi da zababben shugaban kasa, Bola Tinubu a baya.

Auren dole: Wata Matashiya ta yi karar Mahaifinta a kotu

Babban Kwamitin ta gana ne domin duba rahotannin tuntubar da tarukan da aka yi a zababben shugaban kasa, da sauran shugabannin jam’iyyar da masu ruwa da tsaki kan tsarin shiyya-shiyya na rabon mukaman shugabancin majalisar kasa karo ra 10.

“Muna kira ga shugabannin jam’iyyarmu da dukkan ‘yan Najeriya da su ci gaba da kokarin tabbatar da zaman lafiya da ci gaban kasarmu a lokacin da kuma bayan lokacin mika mulki a halin yanzu.” A cewar Morka

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...