Kotun sauraren kararrakin zaben shugaba ta bada tabbacin yi wa kowa adalci

Date:

Daga Safiyanu Dantala Jobawa

 

Kotun sauraron ƙorafe-ƙorafe kan zaɓen shugaban kasa ta fara zama a yau Litinin.

 

An fara zaman ne da misalin ƙarfe 9:15 na safe, inda alƙalin da ke jagorantar zaman kotun, mai shari’a Haruna Tsammani ya gabatar da jawabi.

Tsammani ya ce kotun za ta yi masu ƙarar adalci sannan ya gargaɗi lauyoyi da su guje wa yin kalamai na harzuƙawa.

Bankwana: Ganduje ya yafewa malaman makaranta kudaden gidaje

Ya kuma buƙace su da su bai wa kotun haɗin kai domin ganin an kammala shari’ar cikin lokacin da aka ɗiba.

 

Sauran alƙalan da za su taimaka wajen gudanar da shari’ar sun haɗa da mai shari’a Stephen Adah da Misitura Bolaji-Yusu da Boloukuoromo Moses Ugo da kuma Abbah Mohammed.

 

Gabanin fara zaman, an jibge jami’an tsaro a kan hanyoyin da suke kai wa zuwa kotun.

 

Jam’iyyun adawa irin su PDP da LP ne suka shigar da ƙara suna ƙalubalantar nasarar da ɗan takarar jam’iyyar APC mai mulki, Bola Tinubu ya samu a zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

 

Kadaura24 ta rawaito Sakamakon da INEC ta fitar ya nuna cewa Bola Tinubu na APC ya samu ƙuri’u 8,794,726, sai Atiku Abubuakar na jam’iyyar PDP wanda ya samu ƙuri’a 6,984,520, yayin da Peter Obi na jam’iyyar LP ke biye masu da ƙuri’a 6,101,533.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...