Yan sanda sun kuɓutar da mutane 58 daga hannun masu garkuwa

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Rundunar ‘yan sanda ta Najeriya reshen babban birnin tarayya Abuja, ta ce ta kuɓutar da akalla mutane 58 da aka yi garkuwa da su a dajin Udulu na ƙaramar hukumar Gegu a jihar Kogi, wanda ya yi iyaka da dajin Sardauna dake jihar Nasarawa.

 

‘Yan bindigar da suka fuskanci an fi ƙarfinsu sai suka tsere da harbi da dama a jikinsu, tare da barin mutanen da suka yi garkuwar da su.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ta rabawa manema labarai.

Da dumi-dumi: Yan Sanda a kano sun kama matashin da ya kashe mahaifiyarsa da wuka

Ta ce masu garkuwar da ɓarayin daji sun fara harbin tawagar jami’an tsaron a lokacin samamen da ‘yan sandan suka kai, abin da ya kai ga musayar wuta daga ɓangarorin biyu.

Sanarwar ta ce an samau nasarar ceto mutanen ne sakamakon haɗin giwwar ‘yan sanda da ‘yan sintiri da da mafarauta daga ƙauyuka daban-daban na Abuja, domin daƙile irin waɗannan laifuka da kuma kama masu aikata hakan don gabatar da su a gaban shari’a.

Bankwana: Ganduje ya yafewa malaman makaranta kudaden gidaje

Kwamishinan ‘yan sanda na Abuja CP Haruna Garba ya ce za su ci gaba da aiki tuƙuru domin ceto duk wanda aka ji labarin an yi garkuwa da shi, tare da kama masu wannan aiki.

CP Haruna ya kuma buƙaci mutane da su sanya idanu tare da kai ƙorafin duk wasu mutanen da ba su yadda da sintirinsu ba, ta hanyar wasu lambobin waya da rundunar ta ware.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...