Ranar Yan Jaridu: Zan baiwa yan jaridu damar gudanar da aikin su ba tare da tsangwama ba – Abba Gida-gida

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

Yayin da duniya ke bikin ranar ‘yancin ‘yan jarida, zababben Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, ya bukaci masu kafafen yada labarai da ‘yan jarida da su jajirce wajen bayar da sahihan labarai yayin da suke ci gaba da kare ‘yancin fadin albarkacin baki a cikin al’umma.

Engr. Abba ya ce idan aka samu sahihin rahotanni, kafafen yada labarai za su cigaba da tsare mutuncin su da matsayinsu na masu sa ido a al’amuran da suka shafi al’umma Kuma hakan shi zai basu damar dauke nauyin da aka dora musu.

Da dumi-dumi: Allah kadai yasan jam&l’iyyar da zan mikawa mulkin Kano – Ganduje

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran zaɓaɓɓen gwamnan kano Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu kuma aka aikowa kadaura24.

Zababben gwamnan ya yi kira ga dukkan bangarorin shugabanni da su bayar da gudunmawarsu wajen tabbatar da ‘yancin ‘yan jarida ta hanyar kare hakkin masu aikin yada labarai a duniya.

Engr. Abba Kabir ya ce gwamnatin jihar mai jiran gado za ta hada kai da kafafen yada labarai domin bunkasa rikon amana da shugabanci na gari ta hanyar bayar da bayanai na gaskiya .

Zababben Gwamnan, ya tabbatar wa da ‘yan jarida da al’ummar Kano, cewa a karkashin mulkin sa zai tabbatar da ‘yancin aikin jarida musamman idan ba a tauye mutunci da da’a da ke jagorantar sana’a mai daraja ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...