Jami’a ta dakatar da wani Malami saboda marin wasu dalibai mata

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Jami’ar jihar Imo dake Owerri ta dakatar da daya daga cikin malamanta, mai suna Desmond Izunwanne, bisa zarginsa da mari wasu dalibai mata wadanda suka shiga aji a makare sanye da kayan makarantar sakandire.

Kakakin Jami’ar, Ralph Njokuobi, a wata sanarwa da ya fitar a Owerri, babban birnin jihar, ya ce matakin da malamin ya dauka “abin kunya ne kuma bai dace ba.”

Rashin kishin kano ne zai sa mutum ya rushe Ginin da mukai a tsohuwar Daula Otel – Ganduje

Sanarwar ta ce a taron gudanarwar jami’ar ta amince da dakatar da malamin nan take .

 

Kakakin jami’ar ya kuma sanar da cewa an kafa kwamitin ladabtarwa na mutune uku don “gano musabbabin faruwar lamarin ,” in ji sanarwar.

 

“A karshen taron hukumar gudanarwar da aka gudanar a ranar Talata 2 ga watan Mayu 2023, hukumar ta amince da dakatar da malamin, Dokta Desmond lzunwanne, tare kuma da kafa kwamitin ladabtarwa na mutum uku don bankado dalilan da ya haddasa al’amarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...