Masarautun kano 5 nan gani nan bari – Gwamna Ganduje

Date:

Daga Safiyanu Dantala Jobawa

Gwamnan Jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa Masarautu kano guda biyar da ya ƙirƙiro sun zo kenan sai mahadi ka Ture.
Kadaura24 ta rawaito ana ta rade-radin sabon zaɓaɓɓen gwamnan kano Engr. Abba Kabir Yusuf zai rushe Masarautu da zarar an rantsar da shi a matsayin gwamnan Kano a ranar 29 ga watan mayu.
Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne yayin jawabinsa na ranar bikin ma’aikata ta bana, wanda aka gudanar a filin wasa na Sani Abacha dake kano.
” Mun ƙirƙiro Masarautun nan guda biyar don inganta tsaro, don samar da cigaba, inganta tarihi da samar da kananan burane a kano”. Inji Ganduje
Ganduje ya kara da cewa babu wanda zai rushe wadancan masarautu, sun zama mahadi ka ture Kuma ko mahadin da zai rushe Masarautun ma Allah ba zai kawo shi ba da yardar Allah “.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...