Ƙasar Saudiyya ta gindaya sharuɗɗan fita da Zamzam daga ƙasar

Date:

 

 

Hukumomin filin jirgin sama na Sarki Abdulaziz da ke birnin Jidda na kasar Saudiyya sun sanya sharuda guda hudu ga duk wanda ya yi ziyara yake so ya tafi ƙasarsa da ruwan Zamzam.

Cikin wata sanarwa da aka fitar game da masu ibadar da za su koma ƙasashensu da ruwan zamzam, an haramtawa masu ɗaukar robar ruwan Zamzam a cikin kayansu, sai dai su riƙe shi a hannu a cikin jirgi.

Da dumi-dumi: Kwankwaso ya Magantu a kan batun dawo da Sarki Sunusi II Sarautar Kano

Masu gudanar da ayyukan sun sanar da cewa ko wanene ke son siyan Zamzam sai dai ya siya daga ainihin waɗanda ke siyarwa a wuraren tsayawarsu, kuma lita biyar kawai aka yarda mutum ya ɗauka.

Ko wanne mai ibada ba zai ɗauki sama da roba guda ba ta ruwan Zamzam, kuma sai ya nuna shaidar rijistar umara ta manhajar Nusuk.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...