An harbi jirgin Turkiyya kan hanyar sa ta kwaso ƴan ƙasar a Sudan

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Ma’aikatar tsaron kasar Turkiyya ta bayyana cewa an harbi wani jirgin sojin Turkiyya da ke aikin kwashe ƴan kasar Turkiyya daga Sudan da ke fama da rikici.

 

Jirgin mai lamba C-130 na Turkiyya ya nufi sansanin jiragen sama na Wadi Seidna domin kwashe ƴan kasarsa da ke birnin Khartoum.

Sai dai kuma rahotanni sun bayyana cewa jirgin ya ci karo da harbin kananan bindigogi, a cewar sanarwar da ma’aikatar tsaro ta Turkiyya ta fitar a ranar Juma’a.

Shugabancin majalisa: Abubuwan da aka tattauna tsakanin Tinubu, Akpabio da Barau Jibri

Sanarwar ta kara da cewa, a cewar TRTWorld jirgin ya sauka lafiya, kuma ba a samu wata matsala ba.

 

A yayin mayar da martani kan rahoton, sojojin Sudan sun zargi dakarun sa-kai na Rapid Support Forces, da harbin jirgin sojin na Turkiyya.

 

Sai dai kuma RSF din ta musanta cewa ta harbo jirgin inda ta nace cewa sojojin Sudan na yada karya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...