Yaƙin Sudan: Yadda aka bar wasu daliban Najeriya a Sahara cikin mawuyacin hali

Date:

Daga Umar Sani Kofar Na’isa

 

Wasu daliban Najeriya da ke kan hanyar su ta guduwa daga ƙasar Sudan sakamakon tashe tashen hankula sun makale Sahara a ranar Alhamis.

 

Bayan amince da tsagaita wuta na kwanaki uku da dakarun Sudan da dakarun yan tawayen kasar suka cimma, kasashen na ci gaba da kokarin kwashe ‘yan kasarsu.

Yakin Sudan: An kaiwa daliban Nigeria hari

A ranar Larabar da ta gabata ne gwamnatin Najeriya ta ce ta saki kudi kimanin Naira Miliyan 150 domin daukar hayar motocin bas guda 40 don jigilar wasu ‘yan Najeriya daga Sudan zuwa birnin Alkahira na kasar Masar, inda za a kai su yan Najeriyan.

Yanzu Yanzu: Shugaba Buhari ya halarci Faretin Sojoji Sanye da kakin Soji

Amma wasu daga cikin daliban da aka kwashe sun bayyana cewa suna cikin mawuyacin hali akan hanyarsu ta zuwa kasar ta masar.

Wata daliba da abin ya shafa, wadda ta nemi a sakaye sunanta ta , ta ce direbobin sun sha alwashin ba za su karasa da su kasar masar din ba, har sai an kammala biyansu kudaden da aka yi yarjejeniya da su.

 

“Kafin mu fara wannan tafiya, mun fuskanci abubuwa daban-daban, yanzu haka maganar da nake yi maka mun makale a cikin wata sahara tsawon awanni 5, ba mu san ma Inda muke ba.

“Ba mu da ruwa, Kudinmu ya kare, kuma Direbobin sun ce baza su motsa ko ina da motocin ba,har sai an cika musu kuɗin su dinsu. Mun makale a cikin jeji. Ba mu da komai. Ba mu ma san inda muke ba, kuma muna cikin babban hatsari.”

Sai dai Abike Dabiri-Erewa, shugaban hukumar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje (NiDCOM), ta ce an shawo kan matsalar kuma an ci gaba da aikin kwashe mutanen.

Kimanin ‘yan Najeriya 5,500 ne da suka hada da dalibai suka makale a birnin Khartoum da wasu garuruwan Sudan sakamakon rikicin da ya barke a kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...