Bayan kwanshe makonni a waje, yau Tinubu zai dawo Nigeria,

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

A Yau Litinin ne ake sa ran zaɓaɓɓen shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu zai dawo gida Nigeria.

 

Tinubu zai koma Najeriya ne bayan ya shafe tsawon mako biyar a Paris, inda ya huta, bayan kammala yaƙin neman zaɓen da ya ba shi nasara.

Kifewar kwale-kwale ta yi sanadiyyar Rasuwar Mutane 5 a Kano

Tun farko an tsara cewa zaɓaɓɓen shugaban na Najeriya zai kwan biyu a Paris cikin ƙasar Faransa, daga nan kuma ya wuce zuwa birnin London, kafin ya dangana da ƙasar Saudiyya.

 

Sai dai rashin ganin sa a ƙasar Saudiyya lokacin aikin umra, musamman daidai lokacin da shugaban ƙasar mai barin gado, Muhammadu Buhari yake can, ya haifar da jita-jita da raɗe-raɗi.

Wani mataimakinsa na musamman Bayo Onanuga ne ya tabbatar da rahoton komawar Tinubun Najeriya, ko da yake bai cewa ga taƙamaimai lokacin da zai sauka a ƙasar ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...