Ku guji komawa sabon Allah bayan Ramadan – Malam Dauda ya gargadi al’umma

Date:

Daga Maryam Ibrahim Muhammad

 

Wani Malamin addinin musulunci a Kano Mai suna Malam Muhammad Dauda Lokon makera ya gargadi al’umma da su guji komawa sabon Allah bayan kammala azumin watan Ramadana.

 

” Ramadana makaranta ce da ake son kowa yayi koyi da abubun alkhairin da ya koya, musamman a wuraren Tafsirin Al’qur’ani da sauran wuraren karatuttuka don cigaba da samun yardar Allah S W A”.

Gawuna ya yi wa Musulmi Barka da Sallah, Ya Bukaci su yiwa kasa Addu’ar Zaman Lafiya

Malam Dauda Lokon makera ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da jaridar kadaura24 a Kano.

Abba Gida-gida ya Gargaɗi al’umma game da tukin ganganci, yayin bukukuwan Sallah

Yace an so mutane su cigaba da kasance a yadda suke a watan Ramadana, musamman ta wajen gujewa sabon Allah da kuma taimakawa masu karamin karfi.

 

” Kyauta da sadakar da aka rika yi a watan Ramadana kamata yayi mutane su cigaba, babu shakka idan suka cigaba hakan zai taimaka wajen rage talauci da kuma rage gaba tsakanin mawadata da mabukata “. Inji Malam Dauda Lokon makera

 

Malam Dauda ya yi fatan mawadata zasu dore da yalwatawa marayu da masu karamin karfi a kowanne lokaci don kyautata zamantakewa da kuma neman yardar Allah (S W A).

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...