Ku guji komawa sabon Allah bayan Ramadan – Malam Dauda ya gargadi al’umma

Date:

Daga Maryam Ibrahim Muhammad

 

Wani Malamin addinin musulunci a Kano Mai suna Malam Muhammad Dauda Lokon makera ya gargadi al’umma da su guji komawa sabon Allah bayan kammala azumin watan Ramadana.

 

” Ramadana makaranta ce da ake son kowa yayi koyi da abubun alkhairin da ya koya, musamman a wuraren Tafsirin Al’qur’ani da sauran wuraren karatuttuka don cigaba da samun yardar Allah S W A”.

Gawuna ya yi wa Musulmi Barka da Sallah, Ya Bukaci su yiwa kasa Addu’ar Zaman Lafiya

Malam Dauda Lokon makera ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da jaridar kadaura24 a Kano.

Abba Gida-gida ya Gargaɗi al’umma game da tukin ganganci, yayin bukukuwan Sallah

Yace an so mutane su cigaba da kasance a yadda suke a watan Ramadana, musamman ta wajen gujewa sabon Allah da kuma taimakawa masu karamin karfi.

 

” Kyauta da sadakar da aka rika yi a watan Ramadana kamata yayi mutane su cigaba, babu shakka idan suka cigaba hakan zai taimaka wajen rage talauci da kuma rage gaba tsakanin mawadata da mabukata “. Inji Malam Dauda Lokon makera

 

Malam Dauda ya yi fatan mawadata zasu dore da yalwatawa marayu da masu karamin karfi a kowanne lokaci don kyautata zamantakewa da kuma neman yardar Allah (S W A).

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...