Cutar kansar baki tana kashe yan Najeriya 764 a duk shekara – Gwamnatin Tarayya

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Ministan Lafiya, Osagie Ehanire, ya ce cutar kansar baki da aka fi sani da kansar baka, na kashe mutane 764 a Najeriya duk shekara.

 

Ministan ya bayyana hakan ne jiya a Abuja yayin wani shirin horas da mutane yadda zasu kare kansu daga cutar kansar baka wanda gidauniyar Cleft and Facial Deformity Foundation (CFDF) ta shirya.

Bankwana: Gwamna Ganduje ya nemi afuwar al’ummar jihar kano

Shugabar sashin kula da hakora na ma’aikatar lafiya, Dr Gloria Uzoigwe, ce ta wakilci minjstan, ta ce Najeriya kuma na samun sabbin masu kamuwa da cutar daji guda 1,146 a duk shekara.

 

Ya ce ciwon daji na baki ya kasance daya daga cikin abubuwan da ke haifar da mace-mace mutane masu alaka da cutar daji a Najeriya saboda jinkirin rahoton da ake samu a asibitoci, da gazawar jami’an kiwon lafiya wajen gano cutar da wuri da kuma rashin isar da sako yadda ya kamata da dai sauransu.

 

Ministan ya ce gwamnati za ta kaddamar da wani sabon shirin kula da lafiyar baki a watan Nuwamba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...