A karo na biyu: Abba Gida-gida ya baiwa shugabannin kananan hukumomin Kano shawara

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Zababben gwamnan jihar kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya sake baiwa shugabannin kananan hukumomin jihar kano 44 da sauran manyan ma’aikatansu shawarar kada su kuskure a yi amfani da kudaden kananan hukumomin kan zaben da za’a sake a wasu yankuna a jihar.

 

“Mun da cikakkiyar masaniyar cewa gwamnati Mai barin gado tana shirin fitar da kudada kusan naira Miliyan sittin- sittin zuwa sama domin a yin amfani da su wajen dauko yan daba don su tada hatsaniya a yayin zaɓukan da za a sake a wasu kananan hukumomi a Kano”. A cewar Sanusi Bature

FCE Bichi na daf da durkushewa, saboda matsalolin da suka yi yawa a makarantar – Dr. Hussaini Peni

 

Babban Sakataren yada labaran zaɓaɓɓen gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya aikowa kadaura24.

 

Bayan karbar Sammaci, Rarara ya gurfana a gaban kotu

Yace suna kira ga duk shugabannin kananan hukumomi musamman na Nasarawa da Doguwa da su kiyake bada kudaden saboda gwamnati Mai jiran gado bazata lamunci barnatar da kudaden al’umma ba gaira ba dalili ba.

 

” Ina sanar da duk wadanda wannan shawarar ta shafa da su sani cewa duk wanda ya bari aka fitar da kuɗi da sanin sa to ya Sani zamu daukin matakin ladabtarwa akan sa don haka sai a kiyaye, idan kunne ya ji to gangar jiki ta tsira”. Inji Sanusi Bature

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...