Daga Fatima Kabir Labaran
Kotun sauraron kararrakin zaben majalisar dokokin jihar da ke zamanta a harabar kotun Miller Road da ke Kano ta karbi koken ‘yan takarar majalisar dokokin jihar su 9 na jam’iyyar NNPP Inda suke karar jam’iyyar APC da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC).
Masu shigar da karar sun kuma roki kotun da ta amince da bukatarsu ta neman a basu dama su duba kayan da hukumar zabe ta yi amfani da su a zaɓen da ya gudana a ranar 18 ga Maris, 2023.
Zaɓen Gwamnan Kano: APC ta roki kotun sauraren kararrakin Zabe har abubuwa guda 5
Sun kuma bukaci bayan kotun ta bada izinin duba kayan, ta ci gaba da gudanar da shari’ar akan karar da suka shigar.
Abubuwan da dokar majalisar masarautun jihar kano ta kunsa
Sannan kuma masu karar na jam’iyyar NNPP sun shigar da karar ne a gaban kotu domin kalubalantar batutuwan da suke ganin sun sabawa tanadin dokar zabe ta 2022.
‘Yan takarar jam’iyyar NNPP da suka shigar da karar INEC da APC a kotun sauraren kararrakin zabe, sun hada da, Aminu Saidu Ungogo, Isiyiaku Ali Danja, Abdullahi Ali Wudil Manager, Kabiru Getso Haruna, Mahmud Tajo Gaya, Abdullahi Iliyasu, Musa Adamu Ahmad, Aminu Ibrahim Dambatta, Abdu Ibrahim Madari.
Jaridar AUTHORITY ta bayar da rahoton cewa, an shigar da karar ne a gaban kotu, a ranar 4 ga Afrilu, 2023.