Daga Rahama Umar Kwaru
Rundunar ƴan sanda ta kasa reshen jihar Zamfara ta ce jami’anta sun tarwatsa wani yunƙurin da ƴan bindiga sukai na kai hari a wani ƙauye da ke yankin ƙaramar hukumar Tsafe.
Rahotanni sun tabbatar da cewa jami’an yan sandan sun samu nasarar hallaka ƴan bindigan guda biyu.
Ƙasar Ingila za ta dakatar da daukar ma’aikatan kiwon lafiya daga Najeriya
Sanarwar da mai magana da yawun rundunar a jihar, Mohammed Shehu ya fitar, ta ce lamarin ya faru ne ranar Lahadi, inda aka yi artabu tsakanin jami’an ƴan sandan da kuma maharan.
Rarara ya bayyana dalilan da suka sa yan sandan dake gadin sa su kai harbi
Sanarwar ta ce baya ga waɗanda aka kashe, wasu maharan sun tsere da munanan raunuka a jikin su.