Daga Umar Usman Sani mainagge
Mamallakin zakaran da aka zartar wa da hukuncin kisa a jihar kano, ya ce bai ji daɗin yadda marigayin zakaran da ya haɗa shi faɗa da maƙwabcinsa ba.
Idan za’a iya tunawa kadaura24 a ranar talatar da ta gabata ta rawaito, Mai shari’a Halima Wali a wata kotu da ke Kano ta yanke wa zakaran hukuncin kisa, Inda ta bada umarnin ga mai zakaran da ya yanka shi .
Matakin dai ya zo ne bayan wasu maƙwabtan mai zakaran biyu suka shigar da ƙara, inda suka zargi zakaran da hana su sakat saboda yawan caran da yake yi da zarar sanyin asuba ya kaɗa.
Alhassan Ado Doguwa ya yi Nasara, Kotu ta bada umarnin karasa zaben Tudun Wada da Doguwa
A tattaunawarsa da kafar yada labarai taBBC, mai zakaran, Isiyaku Shu’aibu, mazaunin unguwar Ja’en a birnin Kano, ya ce bai taɓa samun saɓani da makwabcinsa ba a tsawon shekara 20 sai a dalilin zakaran nasa

“Ba zan yi kewar zakaran ba, saboda ba wata shaƙuwa ta ƙut-da-ƙut muka yi da zakaran ba”. Inji mai zakaran
“Yara ne ma suka yanka rigimammen zakaran kafin ma na dawo gida a ranar Juma’a”.
Tun farko, ɗaya daga cikin waɗanda suka shigar da ƙarar, Yusuf Muhammad, ya ce carar da zakaran ke yi, tana shiga haƙƙinsa don kuwa ba ya samun barci cikin kwanciyar hankali da lumana.
Isyaku Shu’aibu ya faɗa wa kotun cewa da ma ya sayi zakaran ne don bikin Easter, inda ya buƙaci kotun ta yi masa rangwame zuwa ranar Juma’a kafin zartas masa da hukunci don amfani da naman a ranar Good Friday, hakan tasa kotun ta amince da bukatar ta shi.
Rahotannin da kadaura24 ta samun sun tabbatar da cewa tuni aka yanka zakaran da Kotun ta bada umarnin yanka shi a ranar juma’ar data gabata.