Yanzu-Yanzu: Ganduje ya kafa kwamitin mika mulki mai mutane 17

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Majalisar zartaswar jihar Kano ta amince da kafa kwamitin mika mulki mai mambobi 17 domin mika ragamar mulki ga gwamnati mai jiran gado a jihar.

 

Majalisar ta kuma amince da wani karamin kwamiti mai mutune 100 wanda za a fitar da bayanai daga ma’aikatu da ma’aikatu da hukumomi daban-daban na gwamnatin jihar kano.

 

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar kano, Malam Muhammad Garba, shi ne ya sanar da hakan lokacin da yake zantawa da manema labarai kan sakamakon taron majalisar na mako-mako da aka gudanar a zauren majalisar da ke gidan gwamnatin jihar Kano, ya ce ana sa ran zababben gwamnan zai ba da wakilai uku a babban kwamitin.

 

Ya ce kwamitin wanda ke karkashin jagorancin sakataren gwamnatin jiha Alhaji Usman Alhaji yana da wadannan mambobi a matsayin shugaban ma’aikatan gwamnati, babban lauya/kwamishanan shari’a, kwamishinan yada labarai, kwamishinan muhalli, kwamishinan kasuwanci da Masana’antu .

 

Sauran sun hada da kwamishinan tsare-tsare da kasafin kudi, kwamishinan kananan hukumomi, kwamishinan ayyuka da samar da ababen more rayuwa, kwamishinan kudi, kwamishinan ilimi, darakta-janar, ofishin kula da filaye, darakta-janar na bincike, Manajan Darakta, Tsare-tsare na Birane da sauransu, hukumar Raya Kasa, yayin da Babban Sakatare, Binciken da Harkokin Siyasa, REPA zai zama sakataren kwamitin.

 

Malam Garba ya bayyana cewa, babban kwamatin zai yi aiki cikin hadin kai da nufin rubutawa tare da mika rahoton mika mulki na karshe cikin makonni uku.

 

Kwamishinan ya bayyana cewa an bai lwa babban kwamitin rikon kwarya umarnin fara shirin mika mulki tare da rubuta nasarorin da aka samu a cikin wa’adin mulki karo biyu na gwamnatin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje.

 

Ya ce kwamitin zai kuma samu tare da tantance rahotanni daga ma’aikatun gwamnati dangane da manyan nasarorin da aka samu, gami da ayyuka/tsari da ke gudana dangane da matakin aiwatar da kasafin kudi, matsaloli, takurawa da dai sauransu daga ranar 25 ga Mayu zuwa yau.

 

Malam Garba ya yi nuni da cewa, an dora wa kwamitin alhakin daidaitawa da gudanar da ayyukan karamin kwamitin kan mika mulki, tattarawa da hada rahotonsu tare da rubutawa da mika rahoton mika mulki ga gwamnati mai zuwa cikin makonni hudu bayan kaddamar da shi.

 

Ya ce gwamna Ganduje zai kaddamar da kwamitin a ranar Talata da karfe 2 na rana a dakin taro na Africa House dake gidan gwamnatin Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...