Daga Maryam Abubakar Tukur
Babban Sakataren yada labaran gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje wato Malam Abba Anwar ya godewa abokin aikin shi yan jarida, saboda irin gudunmawar da suka bashi har ya kai ga samun nasarori Masu tarin yawa a lokacin da yake rike da mukamin babban Sakataren yada labaran gwamna Ganduje.
“A yayin da muke tunkarar karshen wa’adin zango na biyu na mulkin Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje a matsayin Gwamnan Jihar Kano, wanda zai zo a ranar 29 ga watan Mayu, ranar da na dade da sanin zata zo, na ga ya zama dole na gode wa dukkan abokan aikina da na yi aiki da su a tsawon shekaru shida da na yi a matsayin Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamna”. Inji Abba Anwar
Malam Abba Anwar ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya aikowa kadaura24 a ranar juma’ar nan.
Abba Gida-gida ya shawarci masu gine-gine a wararen Gwamnatin kano da su dakata
Yace bayan nada shi a wannan mukami kimanin shekaru 6 kenan da suka gabata “abin da ya fara fadowa a raina, shi ne amanar da shugabana Gwamna ya damka min, wanda har zuwa yanzu bai taba kuka dani akan ta ba, Babu wadanda suka taimaka min na sauke wanann nauyi kamar abokan aikina yan jarida .
Ya godewa Gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje (OFR), bisa damar da ya bashi da kuma kwamishinan yada labarai na jihar Kano Hon. Muhammad Garba wanda ya bada gudunmawa wajen samun nasara ta, ya zama dole in gode da irin shawarar da na samu daga Dokta Sule Ya’u Sule, wanda yayi magana da yawun Malam Ibrahim Shekarau da kuma tsohon shugaban kungiyar Editocin Najeriya Baba Halilu Dantiye (mni). Wanda ya rike Babban Daraktan Yada Labarai, a zamanin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.
“Ba ni da isassun kalmomi da zan yi amfani da su waje gode musu bisa goyon baya da haɗin kan da suka bani, Watakila bazan nuna son zuciya ba idan na ambaci abokan aika wadanda daga cikin su na fito wato Kano Correspondents’ Chapel , da dukkanin kafafen yada labarai da kungiyar yan jaridu ta kasa reshen jihar kano baki daya”.
Duk da cewa sarari na Shugaban Makarantara ne, Gwamna, Kwamishinan Yada Labarai, tsoffin sojoji da abokan aikina, amma ina jin laifi idan ban ambata ba, ban yi tabo da godiya ba, daga zuciyata, ƙaunatacciyar matata da yaranmu.