Ina godiya ga yan jaridu bisa hadin kan da suka ba ni – inji mai magana da yawun Ganduje Abba Anwar

Date:

Daga Maryam Abubakar Tukur

 

Babban Sakataren yada labaran gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje wato Malam Abba Anwar ya godewa abokin aikin shi yan jarida, saboda irin gudunmawar da suka bashi har ya kai ga samun nasarori Masu tarin yawa a lokacin da yake rike da mukamin babban Sakataren yada labaran gwamna Ganduje.

 

“A yayin da muke tunkarar karshen wa’adin zango na biyu na mulkin Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje a matsayin Gwamnan Jihar Kano, wanda zai zo a ranar 29 ga watan Mayu, ranar da na dade da sanin zata zo, na ga ya zama dole na gode wa dukkan abokan aikina da na yi aiki da su a tsawon shekaru shida da na yi a matsayin Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamna”. Inji Abba Anwar

 

Malam Abba Anwar ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya aikowa kadaura24 a ranar juma’ar nan.

 

Abba Gida-gida ya shawarci  masu gine-gine a wararen Gwamnatin kano da su dakata

Yace bayan nada shi a wannan mukami kimanin shekaru 6 kenan da suka gabata “abin da ya fara fadowa a raina, shi ne amanar da shugabana Gwamna ya damka min, wanda har zuwa yanzu bai taba kuka dani akan ta ba, Babu wadanda suka taimaka min na sauke wanann nauyi kamar abokan aikina yan jarida .

 

Ya godewa Gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje (OFR), bisa damar da ya bashi da kuma kwamishinan yada labarai na jihar Kano Hon. Muhammad Garba wanda ya bada gudunmawa wajen samun nasara ta, ya zama dole in gode da irin shawarar da na samu daga Dokta Sule Ya’u Sule, wanda yayi magana da yawun Malam Ibrahim Shekarau da kuma tsohon shugaban kungiyar Editocin Najeriya Baba Halilu Dantiye (mni). Wanda ya rike Babban Daraktan Yada Labarai, a zamanin Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

 

“Ba ni da isassun kalmomi da zan yi amfani da su waje gode musu bisa goyon baya da haɗin kan da suka bani, Watakila bazan nuna son zuciya ba idan na ambaci abokan aika wadanda daga cikin su na fito wato Kano Correspondents’ Chapel , da dukkanin kafafen yada labarai da kungiyar yan jaridu ta kasa reshen jihar kano baki daya”.

 

Duk da cewa sarari na Shugaban Makarantara ne, Gwamna, Kwamishinan Yada Labarai, tsoffin sojoji da abokan aikina, amma ina jin laifi idan ban ambata ba, ban yi tabo da godiya ba, daga zuciyata, ƙaunatacciyar matata da yaranmu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...