Tsarin E-Naira da CBN ya fito da shi zai inganta tattalin arzikin Nigeria – Sarkin Kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, ya jaddda goyon bayansa bisa tsarin e-naira da babban bakin Nigeria da babban bankin kasa CBN na E-Naira, ya bujiro dashi wanda yace zai taimaka wajen bunkasa harkokin Kasuwanci da cigaban kasa.

 

Mai Martaba Sarkin ya bayyana haka ne lokacin da yake karbar bakuncin daraktan CBN shiyar Kano Alhaji Muhd Hamisu Musa yayin da suka ziyarce shi a fadar sa.

 

Sarkin Kano ya taya Abba Gida-gida Murnar lashe zaben gwamnan jihar

Cikin sanarwar da Sakataren yada labaran Masarautar kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa kadaura24, yace Sarkin na Kano ya ce tsarin na E-naira zai tamakawa yankasuwa da sauran al’ummar kasar nan.

 

Sake duba sakamakon zaben gwamnan Kano, APC ta bukaci yan’yan ta su zauna lafiya

Aminu Ado Bayero ya kuma bukaci da babban bakin kasa da ya gyara matsalar network da ake samu yayin hada-hadar kudade, wanda a cewar sarkin yana kawo Nakasu da tarin kalubale da al’umma ke fuskanta.

 

A nasa jawabin babban daraktan bankin Alhaji Muhd Hamisu Musa ya ce sun ziyarci fadar sarkin ne domin shaida masa irin hanyoyin da suke bi wajen wayar da kan alumma amfanin tsarin na E-naira da babban bakin kasa ya bujiro da shi domin taimakawa yan kasuwa.

 

A yayin ziyarar, daraktan na tare da dukkan shugabannin sassa na bankin shiyyar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...